Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa zai zama babban farin ciki a gare ta idan dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya koma jam’iyyar mai mulki ta APC.
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Jam’iyyar na Kasa, Mista Oginni Olaposi, ya fitar ranar Lahadi a Legas.
Olaposi ya mayar da martani ne kan murabus din da Abdullahi Ganduje ya yi daga shugabancin APC da kuma jita-jitar cewa ya yi hakan ne domin ba wa Kwankwaso damar shiga jam’iyyar.
“Kwankwaso ya ci amanar da muka ba shi ta hanyar kokarin kwace jam’iyyar daga hannun wanda ya kafa ta, Dokta Boniface Aniebonam, wanda ya ba shi damar samun tikitin takarar shugaban kasa kyauta a 2023,” a cewar sa.