Daga Comrd. Munir I. Publisher
A siyasa, lokaci ba wai kawai yana bayyana dabara ba ne, har ma yakan tona asirin manufa. Lokacin da Alhaji Buba Galadima ya fara hare-hare kan Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano da kuma Daraktan Hukumar Tsaro ta DSS, hakan bai zo da mamaki ba. Waɗannan hare-haren ba su da tushe balle asali ta fuskar dimokuraɗiyya, sun bayyana ne daidai lokacin da aka cire shi daga kujerar Shugaban Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, mataki na gudanarwa da aka ɗauka a matsayin wani ɓangare na shirin sake fasalin cibiyoyi da inganta aiki ƙarƙashin Kano First Agenda na Gwamna. Sakamakon wannan jerin abubuwa ba mai wahalar fahimta ba ne: ba batun dimokuraɗiyya ba ne, batun takaici ne.
Galadima ya riÆ™e mukaminsa a Kwalejin ne bisa amincewar gwamna, ba bisa wani haƙƙi na kundin tsarin mulki ba. Irin waÉ—annan naÉ—e-naÉ—e na gwamnati, a tsarinsu, suna Æ™arÆ™ashin bita, tantance aiki, da kuma ikon gudanarwa. Shawarar Gwamna Yusuf ta sake fasalin shugabancin Kwalejin, tare da bai wa Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Abdulkadir kujerar shugabanci, amfani ne da wannan ikon domin aiwatar da shirin gyaran cibiyoyi na gwamnati. Babu wani sashe na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, ko Dokar Ilimi (Ƙa’idojin Ƙasa da Kafa Cibiyoyi), ko wata doka da ta bai wa wanda aka naÉ—a haƙƙin riÆ™e mukami har abada ko É—aukar cire shi a matsayin tsanantawa ta siyasa.
Salon da Galadima ya bi abu ne da duk wanda ya daÉ—e yana bibiyar siyasar Nijeriya zai gane nan take. Shiru ko aÆ™alla rashin sukar gwamnati, lokacin da yake kan mukami. Sai kuma, bayan cire shi, a samu kwatsam an gano “mulkin kama-karya”, “murÆ™ushe ‘yanci”, da “rikicin dimokuraÉ—iyya” a cikin gwamnatin da lokacin yana kan mukaminsa bai gano hakan ba. Wannan dole akwai abin tambaya a nan.
Daga cikin abubuwan da suka fi tayar da hankali a ikirarin Galadima akwai yunÆ™urinsa na jingina Daraktan DSS a Kano da abin da ya kira wani shiri na murÆ™ushe ‘yan adawa. Wannan zargi za a iya kwatanta shi da rashin fahimtar kundin tsarin mulki. DSS hukuma ce ta tarayya da aka kafa Æ™arÆ™ashin Dokar Hukumar Tsaro ta Ƙasa ta 1986, tana aiki Æ™arÆ™ashin ikon gwamnatin tarayya, kuma tana ba da rahoto ta hannun Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro. ayyukanta ba sa Æ™arÆ™ashin umarnin gwamnonin jihohi. IÆ™irarin cewa Gwamna Yusuf na ba da umarni ga DSS a Kano kuskure ne mai girma game da yadda tsarin tarayya da tsarin tsaron Nijeriya ke aiki.
Daraktan DSS a Kano ya gudanar da ayyukan hukuma cikin hurumin kundin tsarin mulki da kuma bisa sahihan korafe-korafe. Duk inda aka gayyaci wasu domin amsa tambayoyi, an yi hakan ne bisa damuwa mai tushe a Æ™arÆ™ashin dokokin Nijeriya, ciki har da Dokar Yaki da Laifukan Yanar Gizo ta 2015, wadda ta fayyace iyakar ‘yancin faÉ—in albarkacin baki da kuma laifi a sararin yanar gizo. Kiran waÉ—annan matakai na doka da suna “ramuwar gayya ta siyasa” ba fafutuka ba ce, yin amfani da fahimtar jama’a ne domin manufofi na kashin kai da jam’iyya.
Gaskiyar abin da ake gani a Kano Æ™arÆ™ashin gwamnatin Gwamna Yusuf ta saba da labarin Galadima ta kowane bangare. ‘Yan’adawa na magana da aiki cikin ‘yanci. Kafafen yaÉ—a labarai na gargajiya da na dijital, na aiki ba tare da tsari na takurawa ba. Ayyukan siyasa na gudana a tsakanin jam’iyyu. Ƙungiyoyin farar hula na nan da murya mai Æ™arfi. WaÉ—annan su ne alamomin jiha na gudanar da dimokuraÉ—iyya ba tare da tawaya ba, amma babu batun murÆ™ushe ‘yanci.
A lokaci guda, ayyukan gwamnati suna bayyana kuma suna Æ™aruwa. Manyan makarantun gaba da sakandare na Kano na fuskantar gyaran tsarin da aka daÉ—e ana buÆ™ata. Basussukan gratutoci ga ma’aikatan da suka yi ritaya, waÉ—anda suka taru tsawon shekaru sakamakon sakaci, ana magance su. Tsarin siyasar ubangida wanda a baya ake raba mukamai a matsayin lada na siyasa maimakon cancanta da muradin jama’a, ana rushe shi sannu a hankali. Tabbas waÉ—annan sauye-sauye za su jawo rashin jin daÉ—i ga waÉ—anda tasirinsu ya dogara da tsohon tsari. Amma rashin jin daÉ—in masu gata ba rikicin dimokuraÉ—iyya ba ne. Samun nagartaccen mulki ne.
Al’ummar Kano na daga cikin jama’ar da suka fi fahimtar siyasa da tarihi a Nijeriya. Sun sha ganin sauye-sauyen siyasa masu sarkakiya, sun ga ire-iren wannan siyasar Æ™orafi da ake gani a yanzu, kuma sun kware wajen bambance sukar dimokuraÉ—iyya ta gaskiya da kuma takaicin da aka sake masa suna da “fafutuka”. Wannan hikima ya kamata a yi amfani da ita a yanzu, ba tare da son zuciya ba.
‘Yancin faÉ—in albarkacin baki, kamar yadda Sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulki ya tanada, haƙƙi ne da wannan gwamnati ba ta taÉ“a tauyewa ba. Amma abin da ta yi, kuma za ta ci gaba da yi, shi ne tabbatar da cewa ‘yancin magana ba ya rikidewa zuwa “haƙƙin” yaÉ—a Æ™arya, tayar da rikici, ko gina labaran tsanantawa da ba su da tushe. ‘Yancin magana tabbaci ne na kundin tsarin mulki. ‘Yancin É“atar da jama’a ba haka ba ne. Wannan bambanci ba takura wa dimokuraÉ—iyya ba ne; sharadi ne na rayuwarta.
An zaÉ“i Gwamna Abba Kabir Yusuf ne domin ya yi wa al’ummar Kano hidima, ya gyara cibiyoyinta, ya Æ™arfafa tsarin mulki, ya kuma gina makoma da ta shafi ‘yanÆ™asa, ba cibiyoyin rabon gata na siyasar baya ba. Gwamnatinsa na ci gaba da wannan aiki ba tare da shagaltuwa da hayaniyar masu rikita takaicin kansu da manufar dimokuraÉ—iyya ba.
Tarihi, kamar yadda yake yi a kowane lokaci, zai zana layi mai tsabta tsakanin waÉ—anda suka yi amfani da mukamansu wajen gina cibiyoyi da yi wa jama’a hidima, da waÉ—anda suka juya zuwa kai hari ga cibiyoyin nan da zarar an cire su daga mukamansu. Kano na buÆ™atar siyasa mai zurfi, mai tushe a kan manufa, hujja, da muradin jama’a. Abin da Galadima ke gabatarwa babu É—aya daga cikin waÉ—annan. Kuma al’ummar Kano masu ilimi da balagar siyasa, sun san bambanci.
