Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ne ya tura da tawagar, wadda tsohon shugaban Najeriya, Abdulsalam Abubakar ke yi wa jagoranci.
A ɗazu ne shugaban ƙungiyar Ecowas, Bola Ahmed Tinubu, ya tura wata tawaga zuwa jamhuriyar Nijar domin yin sulhu da sojojin da suka yi juyin mulki.
Hakan na cikin matakan da Ecowas ta cimma a taron gaggawar da ta yi a cikin hutun ƙarshen makon da ya gabata a Abuja.