A bara ne aka kama su kwana huɗu da aikata laifin a birnin Marand. A makon da ya gabata ma hukumomin Iran din sun rataye wasu maza uku, bayan da su ma aka same su da laifin yi wa mata fyade.
Mutanen suna yi wa mata allurar hana jin zafi, bayan sun yaudare su zuwa wani asibitin mai-da-tsohuwa yarinya, ko gyaran jiki na bogi.
Ƙungiyar kare hakkin dan'Adam ta duniya, Amnesty International, ta ce, zuwa yanzu Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan mutum akalla 282, a wannan shekarar kadai, fiye da kowa ce ƙasa a duniya bayan China.
BBC