Zai yi jawabin da misalin ƙarfe 7:00 na safiyar Litinin, 12 ga watan Yuni, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana.
"Ana umartar gidajen rediyo da talabijin da sauran kafofin labarai na intanet su jona daga Gidan Rediyon Najeriya da kuma NTA," in ji sanarwar da Abiodun Oladunjoye ya sanya wa hannu.
A baya dai, ana yin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ne a ranar 29 ga watan Mayu, kafin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya sauya zuwa 12 ga Yuni a 2018.
BBC