Kafafen yada labarai a Najeriya sun ambato kakakin hedikwatar tsaron, Manjo-Janar Edward Buba, yana tabbatar da hakan, lokacin da yake bayani kan kwanton-ɓaunar da aka yi wa dakarun sojin Najeriya a jihar, ranar 14 ga watan Agustan 2023.
Manjo-Janar Buba ya ce har yanzu ana gudanar da bincike kan abin da ya janyo hatsarin jirgin saman rundunar sojin Najeriya a jihar Nejan, ya kuma buƙaci jama'ar gari su kiyaye farfagandar da ƴan bindiga ke yaɗawa a kan batun.
Rahotanni sun nuna cewa ƴan bindiga sun yiwa dakarun sojin Najeriya kwanton-ɓauna inda wasu dakarun suka mutu.
Jirgin rundunar sojin saman Najeriya mai saukar Ungulu, ƙirar MI-171 ya faɗi ne yayin da ya ke kan hanyarsa ta kai ɗaukin gaggawa, a ƙaramar hukuma Shiroro ta jihar Neja.