Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaba Tinubu ya aika wa Obazee, shugaban hukumar masu bayar da rahotannin harkar kuɗaɗe ta Najeriya.
Tinubu ya ce za a binciki CBN da hukumomin da ke da alaƙa da bankin ta hanyar amfani da ƙwararru da hukumomin tsaro da masu yaƙi da rashawa da suka dace don aiwatar da aikin.
Tinubu ya kuma aikewa Obazee kwafin umarninsa na dakatar da Godwin Emefiele a matsayin gwamnan babban bankin.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Emefiele ke fuskantar shari'a kan zargin taimaka wa ta'addanci, sai dai ya musanta zargin.